Tarihin shubannin da Suka mulki Najeriya bayan Samun Yan cin kai - Arewagist.com.ng

Breaking

Arewagist.com.ng

Sayi DATA Ta MTN 1Gig 350, 2Gig 700 3Gig 1k 5Gig 1500 WhatsApp 08122225296

Thursday, October 1, 2020

Tarihin shubannin da Suka mulki Najeriya bayan Samun Yan cin kai

 


Abubakar Tafawa Ɓalewa shine Prime minister na farko daya mulki Najeriya bayan samun Yancin kai yayi shekaru shida yana mulki daga (1960 – 1966)

Rawar da Gwamnatin sa Ta taka.

Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa ya taka muhimmiyar rawa a gwamnatin sa wajen hada kan Kasashen Afrika karkashin kungiya daya Wato African Union (AU) Tareda Tabbatar da cewa Najeriya ta zama kasa mai cin gashin kanta ba Tareda dogaro da wasu ba, Kuma masana sun CE mutum ne mai fadan Ra'ayin sa (Al'ummar sa) a Wuraren taro na kasashe ba Tareda tsoro ba.


Tarihin Najeriya na tsawon Shekara 60 da Samun yancin Kai

https://www.arewagist.com.ng/2020/09/tarihin-najeriya-na-tsawon-shekara-60.html


 


Nmandi Azikwe shine Shugaban kasa na farko a mulkin farar hula, yayi shekaru uku yana mulki daga (1963 – 1966).


Gwamnatin sa ta samu nakasu na rashin cikakken iko a duka Gwamnatocin nasa. 


Tarihi ya nuna cewa Nmandi Azikwe Jajirtaccen dan kishin kasa ne wanda yanada daga cikin waɗan da suka jajirce aka samu yancin kai. 


An tuhumcesa da sanin masaniyar juyin mulkin da aka yi a 1966 wanda ba'a samu nasara ba.


Hutunan yadda akayi Bikin cika Shekaru 60 da Samun Yan cin Kan Najeriya

https://www.arewagist.com.ng/2020/10/hutunan-yadda-akayi-bikin-cika-shekaru.html?m=1



Agunyi Ironsi JTU ya mulki Najeriya amma shi bai dade akan karaga ba Domin duka Watan sa shida akan kujerar mulki daga ( watan Janairu zuwa july na 1966).


Shi ne Shugaban kasa na farko na mulkin Soja kuma A lokacin mulkin sane ya dunkule tsarin mulkin ƙasar zuwa Bai daya, kamar dai yanda aka ga na Hukumomin tsaro wato mataki bayan mataki. 


Rikici ne Ya Haifar da Kafa Gwamnatin sa wadda dududu watan ta shida




Tarihin Yakubu Gowon da ya mulki Najeriya na tsawon shekaru tara 9

 Yakubu Gowon yayi mulki Najeriya tsawon shekaru tara tun daga ( 1966 – 1975 ).

Rawar da Gwamnatin sa ta Taka.

A lokacin Gwamnatin Gowon kafin saukar sa ya Kirkiro jihohi guda goma sha biyu wanda aka saka su karkashin kulawar sojoji. 


Gwamnatin sa ta samu walwala ta kudi a lokaci da aka samu gagarumar riba na man fetur da ake hakowa sannan kuma gwamnatin sa tayi yaki da ma'aikata na tsawon shekara biyu ( 1968 -1970 )


Sai dai  an kalubalanci gwamnatin sa da Almubazzaranci da kudaden da aka samu sanadiyyar man fetur.

Tarihin Najeriya na tsawon Shekara 60 da Samun yancin Kai

https://www.arewagist.com.ng/2020/09/tarihin-najeriya-na-tsawon-shekara-60.html



No comments:

Post a Comment