[[Karanta]] Matansa 4 Sun Ci Amanarsa; Sun Hada Kai Suna Madigo - Arewagist.com.ng

Breaking

Arewagist.com.ng

Sayi DATA Ta MTN 1Gig 350, 2Gig 700 3Gig 1k 5Gig 1500 WhatsApp 08122225296

Sunday, April 7, 2019

[[Karanta]] Matansa 4 Sun Ci Amanarsa; Sun Hada Kai Suna Madigo

Matansa 4 Sun Ci Amanarsa; Sun Hada Kai Suna Madigo

Daga Ibrahim Mustapha, Maiduguri

Wani magidanci ya kama matansa Hudu suna aikata madigo, inda daya daga cikin kannen mutumin ya shaida wa majiyarmu cewa Hakika dan uwansa ya na cikin halin kunci da damuwa har ya kusa haukacewa.

Shi dai mutumin dan asalin jihar Kaduna ne da matan nasa wanda ya ke zama a garin Maidugurin jihar Borno. Uwar gidansa ta shaida wa manema labarai cewa hakika sun rudeta da kudi kimanin naira dubu dari inda ta ce suna sharholiyarsu ne da zaran mijin ya fice kasuwa kuma yaransu sun tafi makaranta.

Ta bayyana cewa, daya daga cikin matan (Amarya) ce ta ja ra'ayinsu izuwa aikata irin wannan mummunar alfashan.

1 comment: