Majalisar wakilai ta yi wa shugabannin tsaro kiran gaggawa - Arewagist.com.ng

Breaking

Arewagist.com.ng

Sayi DATA Ta MTN 1Gig 350, 2Gig 700 3Gig 1k 5Gig 1500 WhatsApp 08122225296

Thursday, June 4, 2020

Majalisar wakilai ta yi wa shugabannin tsaro kiran gaggawa

Majalisar wakilai ta yi wa shugabannin tsaro kiran gaggawa

Majalisar wakilai ta yanke hukuncin yi wa shugabannin tsaro kiran gaggawa sakamakon hauhawar rashin tsaro a kasar na.

Shugabannin tsaron sun hada da: Mai bada shawara ga shugaban kasa a kan tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno, shugaban ma'aikatan tsaro, Janar Gabriel Olonisakin.

Sauran sune sifeta janar din 'yan sanda, Mohammed Adamu da shugaban hukumar tsaro ta farin kaya, Yusuf Bichi.

An yi kiran gaggawar ne bayan bukatar da Sada Soli ya mika gaban majalisar na yin hakan sakamakon hauhawar al'amuran 'yan bindiga a yankin arewa ta tsakiya da arewa maso gabas.

No comments:

Post a Comment