Amurka ta damu game da taɓaɓarewar siyasar Jihar Edo - Arewagist.com.ng

Breaking

Arewagist.com.ng

Sayi DATA Ta MTN 1Gig 350, 2Gig 700 3Gig 1k 5Gig 1500 WhatsApp 08122225296

Saturday, August 8, 2020

Amurka ta damu game da taɓaɓarewar siyasar Jihar Edo

 

Amurka ta damu game da taɓaɓarewar  siyasar Jihar Edo


Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya bayyana damuwa game da "taɓaɓarewar siyasar Jihar Edo", wadda hukumar INEC ke shirin gudanar da zaɓen gwamna a watan Satumba.


"Amurka ba ta ji daɗin abubuwan da ƴan siyasa (a Edo) ke aikatawa ba," a cewar wata sanarwa da ofishin ya wallafa a shainfsa na Twitter ranar Juma'a.


Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka za ta tallafa wa Najeriya wurin tabbatuwar dimokuraɗiyya "matuƙar dai za a riƙa bai wa talakawan Najeriya waɗanda suka zaɓa".


Gwamnan Edo ya ƙwaye Rufin Majalisar Dokokin Edo

https://www.arewagist.com.ng/2020/08/obaseki-ya-cire-rufin-majalisar-dokokin.html


Jijiyoyin wuya sun fara tashi a Jihar Edo da ke Kudu maso Kudancin Najeriya ne bayan rantsar da mambobin majalisar dokokin jihar su 14, waɗanda suka yi yunƙurin karɓe ikon majalisar.


A watan Satumba mai zuwa ne za a gudanar da zaɓen gwamna a jihohin Edo da kuma Ondo.


Amurka ta ce tana kallon Najeriya a matsayin "uwa a Afirka" sannan ta yi kira ga masu ruwa da tsaki ciki har da hukumar zaɓe da su tabbata an yi zaɓen adalci kuma mai cike da zaman lafiya


No comments:

Post a Comment