El-Rufai ya ziyarci makaranta Kurmin Mashi inda aka killace almajirai ‘yan asalin jihar da aka dawo dasu daga jihar Nasarawa su 200.

 nata jawabin kwamishiniyar jin dadin al’umma Hafsat Baba, ta shaida cewa jihar Kaduna ta karbi almajirai akalla 900 daga jihohin Kano, Bauchi, Plateau da Nasarawa.

Sannan kuma gwamnati ta gode wa asusun UNICEF kan tallafa mata da yake yi wajen tufatar da yaran da samar musu da abin da suke nema.