Buhari ya bai wa gwamnoni damar buɗe kasuwanni da masallatai da coci - Arewagist.com.ng

Breaking

Arewagist.com.ng

Sayi DATA Ta MTN 1Gig 350, 2Gig 700 3Gig 1k 5Gig 1500 WhatsApp 08122225296

Monday, June 1, 2020

Buhari ya bai wa gwamnoni damar buɗe kasuwanni da masallatai da coci

Buhari ya bai wa gwamnoni damar buɗe kasuwanni da masallatai da coci

Kwamitin shugaban ƙasa mai yaƙi da cutar korona a Najeriya ya ce za a buɗe dukkanin kasuwanni a Najeriya, yayin da wa'adin farko na mako biyu na sassauta dokar kulle ke cika a yau Litinin.


Sai dai Dr. Sani Aliyu, babban jami'i a kwamitin, ya ce gwamnoni ne za su tsara yadda za a buɗe kasuwannin.

Kwamitin ya bayyana haka ne a wurin taron manema labarai da jami'ansa ke gudanarwa yanzu haka a Abuja.

Sauran batutuwan sune:

Dokar bude jihohin zata fara yau da misalin karfe 10:00pm 

Jirage za su ci gaba da zirga-zirga a tsakanin jihohi daga 21 ga watan Yuni

Haramcin tafiye-tafiye tsakanin jihohi yana nan har sai an sake ji daga gare su.

Dokar hana fita - dake aiki a Abuja da Legas da Ogun - za ta koma daga 10:00 na dare zuwa 6:00 na safe.

Makarantu za su cigaba da kasancewa a rufe.

Otel-otel za su cigaba da harkokin su


No comments:

Post a Comment